A ranar Alhamis din da ta gabata ne ‘yan sanda suka gurfanar da wani mutum dan shekaru 27, Wole Adekunle, a wata kotun majistare da ke Ikeja, a jihar Legas, bisa zargin ya ki biyan bashin Naira Dubu 638,000 na wani Otel.
Ana tuhumar Adekunle, wanda ke zaune a Ayobo, Legas da tuhume tuhume uku Tada zaune tsaye, sata da barazana ga rayuwar Wani ma’aikaci.
Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yan sanda (ASP) Ezekiel Ayorinde ya ce wanda ake kara ya aikata laifin a ranar 10 ga Afrilu, a Otel din Rayban, Ipaja, a Legas.
An yi zargin cewa wanda ake kara ya gudanar da ayyuka marasa kyau a Otel din.
Ayorinde, wanda ake kara anabinshi bashin Naira 638,000 adadin kwanakin da yayi a Otel wanda ya ki biya ba dalili, daga baya yana barazanar kashe manajan Otel din Mista Bamidele Ologun.
Ya ce lokacin da manajan ya nemi kudin sa, sai Fada ya Kaure wanda ake kara ya yi barazanar kashe Manaja muddin ya sake Tambayar sa Kudin.
Alkalin Kotun J. A. Adegun, ya bada Belin wanda ake kara akan kudi Naira 200,000 tare da kawo mutane biyu da zasu tsaya mashi, Mai Shari’a ya ce za a cigaba da Tsare Wanda ake Kara har sai an cika Sharuddan Belin.
Daga Karshe An dage sauraren karar zuwa 16 ga Satumba.