Wata babbar Kotu da ke zamnata a Abuja ta umarci rundunar ‘yan sanda ƙasar nan, da ta saki gawar wasu ‘yan shi’a uku da jami’an rundunar suka kashe, kuma ta biya su tarar Naira miliyan 15.
Kotun ta umarci a mika gawarwakin mabiyan na Shaikh Ibrahim El-Zakzaki ga iyalansu domin su yi masu sutura tare da biyan su diyyar naira miliyan biyar kowannensu.
Sai dai alkalin kotun Mai Sharia Taiwo Taiwo ya yi watsi da bukatar da iyalan ‘yan shi’ar suka shigar na neman rundunar ‘yan sandan ta nemi afuwarsu ta hanyar bugawa a jaridu ba.
‘Yan uwan mamatan da suka hada da Ibrahim Abdullahi da Ahmad Musa da kuma Yusuf Faska da Sa’id Haruna sun shigar da kara ne suna neman a ba su gawar mamatan da ake tuhumar jami’an rundunar da kashewa.
Mamatan wadanda suka hadar da Suleiman Shehu, Mahdi Musa, Bilyaminu Abubakar Faskada Askari Hassan sun gamu da ajalinsu ne a lokacin zanga-zangar lumana da suka yi a Abuja domin neman a saki jagoransu, Shaikh El-Zakzaki.
A lokaci ne ‘yan sanda suka bude musu wuta suka kuma kai gawarwakinsu dakin ajiyar gawa na Babban Asibitin tarayya da ke Abuja a ranar 22 ga watan Yulin 2019.