By Abbas Yakubu Yaura
Wata mata daga birnin Solingen dake yammacin Jamus a ranar Alhamis ta fuskanci hukuncin durin shekaru 15 bayan da aka same ta da laifin kashe biyar daga cikin ‘ya’yanta shida.Yaran wadanda suke tsakanin shekara daya zuwa shekara takwas.
Kotun dake zamanta a birnin Wuppertal, bata sami wani dalili ba, wanda kusan hakan ya haramta sakin matar, mai shekaru 28, bayan ta shafe shekaru 15 a matsayin wacce ta saba.sai dai kuma babban dan matar ya tsira daga munanan ayyukan nata.
A lokacin da ake gudanar da shari’ar, mai gabatar da kara ta yi zargin cewa sai da ta fara yi wa yaran kalaman kwantar da hankali sannan ta shake su daya bayan daya har sai da suka mutu.
Jami’an binciken sun yi imanin cewa ganin hoton mijinta tare da wata sabuwar abokiyar zama shi ne lamarin daya tunzura ta wajen aikata laifin, wanda ya girgiza Jamus.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa matar ta aika masa da sakon cewa ba zai kara ganin yaran ba, lamarin dai ya faru a ranar 3 ga watan Satumba na shekarar 2020.
Matar ta dage cewa wani ne ya kutsa kai ya shiga cikin gidanta, ya daure ta sannan ya tilasta mata ta rika aika sakonnin hira kafin ta kashe yaran, kwararrun masu tabin hankali sun gano cewa babu wata shaida dake nuna cewa tana da tabin hankali.
Lauyan dake kare ta ya bukaci a sake ta ne bisa hujjar cewa akwai shakku kan ko wanda yake karewa ta aikata kisan.
Kotun ta gano cewa mahaifiyarsu ta kashe Melina mai shekara 1, fa Leonie mai shekaru 2, sai Sophie 3, da Timo 6, da Luca, mai shekaru 8, wacce daga bisani ta jefa kanta a gaban jirgin kasa a tashar tsakiya ta Dusseldorf amma ta tsira.
Sai dai kuma Ta aiki babban danta, wanda ya tsira daga harin nata ba tare da wata matsala ba,zuwa wurin kakarsa.