Kotun sauraren kararrakin zaben ‘yan majalisa dake jihar Filato ta yi watsi da karar da dan takarar Sanata a jam’iyyar APC ya shigar yana mai kalubalantar zaben dan takarar Sanata a jam’iyyar PDP mai wakilar Filato ta Arewa.
Kotun ta tabbatar da Sanata I.D. Gyang na PDP, inda ta yi watsi da karar Sanusi Mohammed Inuwa na APC.
Sannan har wala yau kotun ta yi watsi da karar da dan majalisar wakilai na PDP wato Timothy Golu ya shigar da na APC Yusuf Gagdi, dan majalisa mai wakiltar Pankshin/Kanke/Kanam a Filato din.
Da yake yanke hukunci, mai shari’a Theophilus Nzeugwu, ya ayyana Gyang a matsayin zababben da ya lashe zabe a ranar 23 ga watan Fabarairu. Mai shari’ar ya ce karar Mohammed Inuwa akan Sanata Gyang ba ta da hurumi, kuma a don haka ta yi watsi da bukatarsa.