Kotun daukaka kara da ke Abuja ta yi fatali da karar da wani bangare na jam’iyyar APC reshen jihar Sokoto ke kalubalantar bangaren zartarwar jam’iyyar a jihar.
Wani kwamitin mutane uku na alkalai karkashin jagorancin mai shari’a Williams Daudu a hukuncin ya bayyana cewa kararrakin uku ba su da inganci kuma ba su dace ba.
Kwamitin ya ci gaba da cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar ne ba aikin kotu na tantance shugabannin jam’iyyar siyasa ba.
Kwamitin ya ce kotun za ta iya shiga tsakani ne kawai a cikin al’amuran da sashe na 285(14) (C) ya shafa, wanda ke magana a kan laifuffukan da suka taso daga zaben fidda gwani na fitar da ‘yan takara.
KARANTA WANNAN LABARIN: An tsaurara jami’an tsaro a kwayar birnin Kano, tare da rufe wasu hanyoyi
Kwamitin, a hukuncin, mai shari’a A.B. Mohammed, ya ci gaba da cewa, babbar kotun tarayya da ke Sokoto, wadda tun farko ta yi watsi da karar, bisa dalilan da ta hana ta yin la’akari da tanadin sashe na 285(9) na kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999, wanda aka yi wa kwaskwarima, ba ta da hurumin shigar da kara.
Wasu ‘yan jam’iyyar APC da suka fusata, Mainasara Abubakar Sani Rabi’u Ibrahim da Aminu Ganda sun shigar da karar suna kalubalantar amincewa da Isa Sadiq Acid da Hassan Bello a matsayin jami’an jam’iyyar na jiha.
Hakan ya biyo bayan gudanar da majalissar guda biyu ne, wadanda suka amince da bangarori daban-daban a matsayin shugabannin jam’iyyar a jihar Sokoto.
A wani labarin kuma na daban
Ina Goyon Bayan Yunkurin Tsige Shugaba Buhari— Gwamna Ortom
Gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom ya yabawa majalisar dokokin kasar nan dangane da baiwa shugaban kasa Muhammadu Buhari wa’adin makonni shida na kara kaimi wajen yaki da rashin tsaro ko kuma su iya tsige shi.
A ranar Talata, 27 ga watan Yuli, 2022, jam’iyyar PDP, majalisar dattawa karkashin jagorancin shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Philip Aduda, ta fice daga zauren majalisar domin nuna rashin amincewa da gazawar shugaban kasa Muhammadu Buhari na kawo karshen rashin tsaro a Najeriya.
Daga baya Aduda da takwarorinsa sun yi jawabi ga kungiyar ‘yan jarida ta Majalisar Dattawa inda suka ba da wa’adin makonni shida da su ka fara shirin tsige Shugaba Buhari idan ya kasa kawo karshen rashin tsaro a kasar.
Gwamna Ortom ya yi wannan yabon ne a ranar Juma’a, 29 ga Yuli, 2022 a masaukin Gwamnan Jihar dake Abuja, a lokacin da ya karbi tawagar wasu ‘yan Majalisar Dokoki ta kasa karkashin jagorancin Aduda da suka zo yi masa bayani kan lamarin.
Gwamnan ya bayyana matakin da majalisar dattawa da ta wakilai suka dauka na tsige shugaban kasar a matsayin hali irin na masu kishin kasa, kuma ya yabawa wasu ‘ya’yan jam’iyyar APC mai mulki da suka zabi yin abin da ya dace.
A cewar Ortom, Buhari ya yi kasa a gwuiwa da yadda ‘yan Najeriya ke zato wajen magance kalubalen tsaro da shawo kan tabarbarewar tattalin arzikin kasar nan, don haka akwai bukatar a ba da dama ga mutum wanda ya cancanta.
Tun da farko Aduda ya shaida wa Ortom cewa a matsayinsa na shugaban jam’iyyar PDP a yankin Arewa ta tsakiya, tawagar ta ga ya dace ta yi masa bayani kan matakin da majalisar dokokin kasar ta dauka na tsige shugaban kasar.
Ya shaida wa Gwamnan cewa duk da cewa Majalisar Dattawa ce ta fara yunkurin tsige shi, amma Majalisar Wakilai da kuma dimbin ‘ya’yan Jam’iyyar APC sun shiga cikin wannan yunkuri.
Ziyarar Aduda ya samu halartar Sanata Orker Jev da Hon Samson Okwu da dai sauransu