Kotun Koli ta Nijeriya ta bayyana Sanata Hope Uzodinma na jam’iyyar APC a matsayin gwamnan jihar Imo, inda ta sauke gwamna mai ci Emeka Ihedioha na jami’iyyar PDP
kotun ta bayar da umarnin fitar da gwamna Emeka daga gidan gwamnati nan take, sannan ta kuma umarci hukumar zabe ta mika shaidar lashe zabe ga Hope Uzodinma a kuma rantsar da shi ba tare da bata lokaci ba.
Kotun ta Koli ta mayarwa APC wasu kuri’u da aka soke mata yayin zaben, inda tace ya kamata a daura su a kan kuri’un da APC din ta samu.
Gaba daya Alkalan kotun bakwai sun amince cewa hukumar zabe INEC ta yi kuskure wajen soke kuri’un da APC din ta samu yayin zaben.