Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayar da tabbacin cewa ba za ta shiga tsakani ba a zaben 2023, domin ba ta da wani dan takara ko jam’iyyar siyasa da take goyan baya.
Shugaban Hukumar Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka jiya a Abuja a wajen taron tunawa da Abubakar Momoh karo na 4 kan ‘Dokar Zaben 2022: Mahimmancin Jam’iyyun Siyasa da Babban Zaben 2023.
An shirya laccar ne domin karrama tsohon Darakta-Janar na Cibiyar Zabe (TEI), Marigayi Farfesa Abubakar Momoh wanda ya rasu a ranar Dimokradiyya, 29 ga Mayu, shekarar 2017.
Yakubu ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa kuri’unsu ne kawai za su tabbatar da sakamakon zaben 2023 da kuma zabukan da za a yi a fadin kasar nan, a nan gaba.
Jaruman Ma’aikatar Nollywood da aka sace sun shaki iskar ‘yanci
Yakubu wanda Shugaban sashen TEI Farfesa Abdullahi Abdu Zuru ya wakilta, ya kuma jaddada bukatar masu ruwa da tsaki, musamman jam’iyyun siyasa da su lura da manyan abubuwan da sabuwar dokar zabe ta 2022 ta bullo da su da kuma yiwuwar tasirin wadannan sauye-sauyen kan zabe mai zuwa. .
Ya ce an kirkiro sabbin fasahohin ne domin zurfafa harkokin zaben kasar.
“‘Tsaro ya fi damuwa fiye da jefa kuri’a'” inji shi.