Ku baiwa ƴan Najeriya masu Fasfo daya ƙare damar dawo wa gida — Aregbesola ga Immigration
Ministan Harkokin Cikin Gida Rauf Aregbesola ya umarci Hukumar Kula da shige da Fice NIS dasu baiwa ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje damar dawo wa gida, tare da fasfon su daya lalace.
Da yake maida jawabi ga wani Ɗan Najeriya dake Zaune a Amurka, Mr. jamui Kasumu, Aregbesola ya bada umurnin a ranar Laraba a ofishin fasfo na Alausa dake Lagos.
An gano cewa Kasumu yayi Ministan ƙorafi cewa Ofishin Hukumar dake Amurka da Delta sun hana shi dawo wa Najeriya saboda yana da fasfo daya lalace.
KARANTA WANNAN LABARIN: Kotu Ta Kori Karar Da Aka Shigar Kan Oyetola Na Rashin Cancantar Sa A Matsayin Dan Takarar APC
Yace ya samu damar dawo wa gida bayan ya samu shaidar tafiye-tafiye bayan ya same shi ta hanyar danganta da Najeriya, inji Jaridar Star.
Aregbesola yace ƴan Najeriya mazauna Ƙasashen Waje suna da damar dawo wa da fasfo na Najeriya daya lalace, ko kuma na wasu ƙasashen.
Yace babu wani ɗan Najeriya dake buƙatar shaidar tafiye-tafiye, sai dai waɗanda ɗiyansu ba ƴan Najeriya bane.
Ya kuma buƙaci Ƴan Najeriya masu zama a kasashen waje dasu canja fasfo nasu, domin samun dama.