Gwamnatin Tarayya ta bukaci al’umma da su fifita kare lafiya da rayukansu sama da hankoron ganin gwamnati ta janye dokar takaita zirga-zirgar da ta kafa don dakile yaduwar annobar Korona.
Sakataren gwamnatin Nijeriya kuma shugaban kwamitin yaki daKorona, Boss Mustapha ne ya bayyana hakan, inda ya ce, gwamnati na da shirin sake bude harkokin tattalin arziki kamar da, amma sai jama’a sun kiyaye sharuddan da kwararru suka gindaya don kare yaduwar annobar.
Rfi Hausa ta labarto cewa; Wannan na zuwa ne bayan da gwamnatin ta yanke shawarar daukar matakin cigaba da takaita harkokin yau da kullum da hana zirga-zirga tsakanin jihohi, da karin makwanni 2.
A halin da ake ciki, cibiyar yaki da yaduwar cutuka ta Najeriyar NCDC, tace adadin wadanda suka harbu da cutar coronavirus a fadin kasar ya haura zuwa dubu 6 da 401, bayan samun karin mutane 226 da suka kamu da cutar a jiya Talata, yayinda adadin wadanda suka mutu ya kai mutane 192.