Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari ta shawarci iyaye da su kara kwazo wajen tarbiyyar ‘ya’yansu saboda a cewarta hakan zai magance barna a cikin al’umma.
Uwargidan ta bada shawarar ne a ranar Litinin a wani taron addu’a na musamman da ta shirya don yi wa kasa addu’a a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Taron an yi mishi take da: “Muhimmancin addu’a wajen samun saitin jagorancin kasa”.
Uwar gidan shugaban kasan ta ce rashin tarbiyar yara ne tushen rikice-rikicen da ke addabar Nijeriya.
“Yau, mafi yawan matsalolin da suke fuskantar kasar nan sakamakon rashin tarbiya ne da iyaye basa yi sannan da soyayya, kula da girmama juna.
“Zuri’ar da ta ginu akan soyayya da kula da kuma samar da du wani abin da ake bukata tafi kowa damar koya wa sauran mutanen da suke rayuwa dasu a cikin al’aumma haka.
“Ina kira ga iyaye da su farka don sauke nauyin da ya hau kansu ta hanyar samar wa da ‘ya’yanmu yanayi mai kyau wanda hakan zai magance matsalalolin da suke damunmu yau da kullum,”
Ta sake kira ga ‘yan Nijeriya da su kasance masu neman taimakon ubangiji a kullum akan al’amuran da suka shafi kasarsu.
“Yana da muhimmanci lokaci bayan lokaci, mu rika tuna manufar rayuwarmu, wanda shi ne bautar mahaliccinmu mu rika koka mi Shi.
“Yakamata mu kara kokari a kan abubuwan da suka shafi jin dadin iyalanmu, musamman ma da ya zama gwamnati ta bada damar yin hakan.
“Mun raba kafa a fannin tattalin arziki, mun shiga noma da wasu harkokin da ban a man fetur ba. Akwai shirye-shirye na more rayuwa da wasu basuka da zasu inganta rayuwar ‘yan kasa wanda kuma kowa zai iya samu.
Uwar gidan ta nemi mahalarta taron da su kwaikwayi koyarwar Annabi Muhammadu (s) wajen habaka zaman lafiya da kauna a tsakanin mabiya addinai a kasar.
Ta kuma bukaci ‘yan Nijeriya da su yi addu’a don ganin bayan wasu matsalolin tattalin arziki da tsaro da kasar take fama da su.
Manyan malaman addinin Musulunci sun halarci taron addu’an.