Shugaban kasa Muhammdu Buhari ya gargadi Musulmai game da shiga ayyukan ibadar da ka iya zama silar kamuwa da cutar COVID-19 a kasar, a daidai lokacin da aka fara gudanar da azumin watan Ramadan a wannan Juma’a.
Cikin wata sanarwa da Kakakin shugaban kasar, Garba Shehu ya fitar, shugaba Buhari ya bukaci Musulman da su kauce wa taruwar jama’a wajen bude-baki da sallar jam’i, matakin da kasashen Musulmi na duniya suka dauki irinsa.
Buhari ya bayyana azumin bana a matsayin mai tattare da kalubale, lura da cewa, ya zo ne a cikin wani yanayi da duniya ke fafutukar yaki da cutar coronanvirus.