Tsohon Shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan ya gargadi ‘yan siyasar kasarnan da su yi kokari su kaucewa duk wani yunkurin da zai haifar da tashin hankali da kawo cikas ga zaman lafiyar kasarnan. Inda har wala yau GEJ ya roke su akan a maimaikon haka su rungumi hanyar inganta zaman lafiya da ci gaban kasa.
Jonathan ya bayyana hakan ne a yayin da yake jawabi ga taron shugabannin Kabilarsa ta Ijaw, inda ya ce ya zama wajibi ‘yan siyasa a daidai wannan lokacin su sanya ci gaban kasa a gaba fiye da komai, domin a cewarsa abin da siyasa ke bukata ke nan; “ba wai raba kan jama’a ko kuma yaki da abokan gaba ba.” Inji shi.
Tsohon shugaban kasar ya ce a matsayinsa na mai fafutikar ganin dimokuradiyya da shugabanci nagari ya wanzu a Nijeriya da ma Afirka baki daya, bukatarsa ita ce ganin jama’arsa sun taka gagarumar rawa wajen zabin wanda zai jagorance su da kuma yadda ake jagorancin.