Kwamandan rundunar sojojin Najeriya na Operation Hadarin Daji, Manjo Janar Jide Ogunlade, a yau Talata, ya bai wa ‘yan bindigar da suka addabi jihar Zamfara umarnin su mika wuya ko kuma su fuskanci fushin rundunar.
Manjo Janar Jide, ya sanar da wannan gargadin ne lokacin taron manema labarai da aka yi a hedkwatar rundunar da ke Gusau babban birnin jihar.
Kwamandan, ya nuna rashin jin dadinsa game da yadda ‘yan bindigar suka ki mika wuya, tun bayan rantsar da sabon Gwamnan jihar Alhaji Bello Matawalle, inda ya ce za a yi wa wadanda suka tuba suka mika wuya afuwa.
A cikin lokuta kadan mun samu rahoton hare-hare da suka kai 20 a unguwanni daban-daban a jihar.