Kungiyar ‘Arum Cultural and Development Association (ACDA)’ dake jihar Nasarawa ta bukaci ‘yan Nijeriya da su rungumi juna domin zama cikin zaman lafiya, ta hanyar nuna wa juna soyayya inda suka ce ta hakan ne kawai za a samu ci gaba da bukasar kasa.
Sabon shugaban kungiyar, Mr Emmanuel Ajah, shi ne ya yi wannan kira a ranar Litinin bayan da aka kammala zaben shugabanin kungiyar a garin Arum Sarki, dake yankin ci gaban kasa na Nasarawa.
Ajah ya kara da cewa, zaman lafiya na da matukar muhimmanci ga ci gaban kasa a dukkan matakai a saboda haka ya kamata a fuskanci wannan akida.
Ya kuma mika godiyarsa ga ‘yan kungiyar bisa yadda suka zabe shi a matsayin shugaban kungiyar ya kuma yi alkawarin samar da ci gaba da hadin kai ga dukkan ‘yan kungiyar don samun ci gaban da ya kamata.
Akan haka ne shugaban kungiyar ya nemi hadin kan dukkan ‘yan kungiyar don samar da cigaban da ake bukata. Ya kuma yi alkawarin tafiya tare da dukkan ‘yan kungiyar a zamanin shugabancinsa.