Kungiyar Inyamurai ta Ohanaeze Ndigbo ta bukaci gwamnonin yankin kudu da su sanya baki don ganin an sako shugaban Inyamurai ta IPOB Mazi Nnamdi Kanu.
Kungiyar ta ce ya kamata gwamnonin su yi la’akari da sakamakon da shari’ar Nnamdi Kanu za ta haifar a yankin na kudu muddin aka fara ta a 26 ga watan Yuli.
Kazalika ta ce ya kamata a yi fargar jaji musamman bangaren magoya bayansa na ganin aun guje wa duk wani nau’in zanga-zanga ganin cewa za a iya fuskantar kalubale da dama.
Cikin wata takarda da Sakataren Ƙungiyar ta Ohanaeze wato Mazi Okechukwu Isiguzoro ya fitar, ta ce ba za ta iya hana magoya bayan Kanu bazama tituna ba muddin aka fara shariar tasa.
Ya ce yanzu haka idan da a ce akwai kara bai kamata gwamnonin su gaza kuɓutar da Kanu ba duba da irin karamci da ya yi musu na Kin bijirewa.
Comments 1