Onuoha, yana bayani ne taron gangamin girbi na shekarar 2019 a unuguwar Garki dake Abuja, ya ce dokar za ta haifar da karin matsala ce kawai maimaimakon gyara da ake neman yi.
Ya kuma bayyana cewa, rayuwar al’umma da nada matukar mahimmanci, kuma dauka rai aiki ne na Allah madaukakin Sarki saboda haka bai kamata a bari a kashe mutum haka nan kawai ba, saboda haka kisa ba zai yi maganin kalaman batanci ba.
”Muna da manyan mastalolin dake damun al’umma, tun daga harkar wutar lantarki rahsin kyawun hanyoyi, anan ne ya kamata gwamnati ta mayar da hankalinta ba maganan kalaman batanci ba.
”Idan mutane basu samu abin da suke nema daga gwamnati ba dole su yi magana, bai kamata a nemi toshe bakuna jama’a ba.
Wannan magaman da al’umma suke yana nuna gazawar gwamnati ne, talakawa suna da ‘yancin kai kukansu da kuma kokawa akan lamarin da basu gane ba.
”Maimako maganar kalaman batanci ya kamata majalisa ta mayan da hankalinta zuwa dokokin da za su fafarfado ta rayuwar al’ummar Nijeriya gaba daya.