Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara ya amince da bayar da fili domin kafa jami’ar Alkur’ani da Musulunci a jihar.
Kungiyar Atta’arif Fil-Islam Charity Organisation, mai shedikwata a Jeddah, da ke kasar Saudi Arabiya ce za ta kafa jami’ar.
Sanarwar da gwamnati ya fitar a Gusau a ranar Lahadin nan ta hannun Malam Nasiru Biyabiki, ta ce Matawalle ya bayyana hakan ne a wata liyafar cin abinci da aka yi a Jeddah na kasar Saudiyya.
Matawalle ya samu wakilcin kakakin majalisar dokokin jihar Alhaji Nasiru Magarya.
Wanda ya kafa kungiyar agaji kuma limamin Masjidur-Rahma, da ke Jeddah, Farfesa Shekh-Khalid Alhammudy, ya ce jami’ar za ta ciyar da harkar ilimi gaba a jihar da Najeriya.
“Kungiyar ba da agajin tana aiki tare da haɗin gwiwar sauran ƙungiyoyin ‘yan’uwa da hukumomin gwamnati don samar da cibiyoyin horo da sauran muhimman ayyuka a faɗin ƙasashen Afirka.
Alhammudy ya ce “Waɗannan wasu tsare-tsare ne na kare al’umma waɗanda ke tallafawa ƙasashe masu tasowa don cimma burinsu.”
Malamin addinin Musuluncin ya yi alkawarin ci gaba da yi wa Zamfara da Najeriya addu’a domin samun dauwamammen zaman lafiya da ci gaban addini da tattalin arziki.
A nasa martanin, Matawalle ya godewa kungiyar bisa wannan karamcin tare da yin alkawarin gwamnatin Zamfara zata ci gaba da inganta jami’ar.
“Yana daga cikin ka’idojinmu don maraba da duk wani ci gaba, musamman wanda ke da tasiri kai tsaye ga jiharmu da kasa baki daya,” in ji gwamnan. (NAN)