By Abbas Yakubu Yaura
Kungiyar Kiristocin Najeriya tace wasu ‘yan bindiga sun sace wasu masu ibada 66 a ranar Lahadi, 31 ga watan Oktoba, 2021, a cocin Emmanuel Baptist dake Kakau Daji a karamar hukumar Chikun ta jihar Kaduna.
Kungiyar tace sabanin adadin da aka bayar a baya a binciken data gudanar ya nuna cewa an yi awon gaba da jama’a 66 inda aka farmakesu da bindigogi, sannan kuma an harbe wani mutum guda a yayin da ake tsaka da gudanar da ibadar cocin.
Mataimakin shugaban kungiyar ta CAN a jihohin Arewa 19 da kuma Abuja, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar a jihar Kaduna, Rabaran John Hayab, ya bayyana haka a wata hira da yayi da jaridar PUNCH ranar Asabar.
“Lamarin ya faru ne da misalin karfe 10 na safe a yayin gudanar da ibada a ranar Lahadi 31 ga watan Oktoba.
“A yayin wannan kazamin harin, an kashe mutum daya yayin da wani daya ya samu rauni wanda a yanzu haka ke samun kulawa likitoci a asibiti.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa “Daga cikin mutanen da aka sace akwai yara, mata masu shayarwa, mata masu juna biyu, tsofaffi da matasa maza da mata.
“Kalubale na rashin tsaro a Kaduna bai inganta ba, kuma cocin ya kasance abin ya shafa. Ga dukkan alamu gwamnatin jihar Kaduna bata da karfin tafiyar da lamarin.”a cewar Hayab
Kungiyar “CAN ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta gaggauta daukar mataki kafin kalubalen rashin tsaro a jihar Kaduna ya jefa al’ummar kasar cikin babbar matsala.”