By Abbas Yakubu Yaura
A ranar Asabar din da ta gabata ne kungiyar kiristoci ta Najeriya ta yi korafin cewa dalibai hudu na kwalejin Bethel Baptist dake Kaduna sun shafe tsawon kwanaki 120 a hannun ‘yan bindiga bayan sace su watanni hudu da suka gabata.
Don haka kungiyar ta yi kira ga gwamnati da ta rubanya kokarinta na kawo karshen aikata laifuka a kasar.
Mataimakin shugaban kungiyar ta CAN na (jihohin Arewa 19 da Abuja) da shugabanta na jihar Kaduna, Rabaran Joseph John Hayab ne suka bayyana hakan a wata sanarwa mai taken ‘Daliban Makarantar Sakandare na Baptist ta Kaduna har yanzu suna hannun ‘yan bindiga sama da kwanaki 120 a yau.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Abin takaici ne a sake tunatar da mu cewa duk da matakan tsaro daban-daban da gwamnati ta dauka a jihar Kaduna, yaranmu da ke makarantar sakandare ta Bethel Baptist da aka yi garkuwa da su tun ranar 5 ga watan Yuli, 2021 a harabar makarantar da ke Damishi, Kaduna. har yanzu ba a sake su ba.
“Iyaye, masu kula da makarantu, shugabannin coci da wadanda suke da alaƙa sun damu. Mun yi addu’a kuma muna ta addu’a. Mun yi kira da kai ku kanmu ga gwamnati da wadanda muke ganin su ne alhakin tsaron al’ummarmu amma tafiyar ‘yanci ga yaran mu ta kasance tana tafiyar muciji.
“Don haka ya kamata gwamnati ta rubanya kokarinta na ganin ta dakile barnar da wadannan miyagu ke haddasawa ‘yan kasa,” inji ta.A halin da ake ciki rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta ce ana kokarin ceto sauran daliban ba tare da samun wani rauni ba.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mohammad Jalige, a wata tattaunawa da ya yi da daya daga cikin ‘yan jaridu, ya ce jami’an rundunar na yin duk mai yiwuwa don ganin sun ceto daliban da sauran mutanen da ke hannun masu garkuwa da mutane a fadin jihar.