Daga Uzairu Dauda Bunga
Kungiyar sa ido kan babban zaben Najeriya ta kasashen turai a 2019, ta bayyana zaben zagaye na biyu a jahar Kano da cewa,anyi shine sakamakon kin amfani da na’uarar tantace masu zabe card reader da kuma yin zabe fiye da yawan masu kada Kuri’a a zaben Gwamna dana ‘yan majalisar dokokin jahar na ranar 9 ga watan Maris 2019.
Shugabar tawagar sanya ido kan babban zaben, Marie Arena, lokacin da take gabatar da rahoton karshe a otel din Transcorp Hilton Abuja ranar Asabar, ta lura cewa zaben karo na biyu an gudanar da shine Saboda soke wasu runfunan zabe a watan na Maris.
“Hakan ya sanya aka sanar da zaben a matsayin wanda bai kammala ba sakamakon yawan runfunan zabe da aka soke a watan Maris, da kuma yawan Kuri’un da suka zarce masu kada Kuri’a da ya wuce tazarar da aka samu. Hukumar Zabe mai zaman kanta ta bayyana soke zaben a dalilin hatsaniya, rashin dada da kin amfani da na’uarar tantace masu zabe card reader.
“Ba abi tsarin tantacewa na zamanin ba idan na’ura taki tantace yatsu yadda yakamata ba. Ba a kare tsarin sirrinta akwatin zabe ba yadda ya dace a kusan daya bisa ukun runfunan zaben da aka sanya ido,” a cewarta.
Game da tsarin da aka gudanar da zaben zagaye na biyu kuwa, Kungiyar kasashen turan ta bayyana cewa hukumar zabe ta inganta shirye shiryen ta na sanya kayan aiki da wuri a kusan dukkanin runfunan zaben da aka sa ido, sai ta Kara da cewa anbi dukkanin ka’idodji a runfunan zabe guda 40 da tawagar Turai suka sanya ido.”
Tayi nuni da cewa an karbi sakamakon zaben Kananan Hukumomi biyu daga cikin Kananan Hukumomi 29 a jahar Kano da aka maimaita zaben a hedikwatar hukumar zabe sakamakon matsalar tsaro. Masu sanya idon na kasashen Turai, sun ziyarci cibiyoyin tattara sakamakon zabe guda 12, sun kuma lura da Wakilan Jam’iyyu suna wajen. Tawagar sanya idon ta Turai sunce anbi dukkan ka’idodji na karbar sakamakon cikin adalci.”
Arena tace an samu gagarumin cigaba a Najeriya fiye da zabukan da suka gabata a cikin kasar duk da cewa akwai guraren da suke neman gyaran gaggawa don kaucewa sake faruwar lamarin, ta kara da cewa shawarwarin da Kungiyar Turai suka bayar a zaben shekara ta 2015 anyi aiki dasu a wadannan zabukan 2019.