Kungiyar ƙwadagon ta NLC ta yi kakkausar suka ga gwamnatin tarayya game da ƙarin farashin mai da kudin lantarki, tana cewa wahalar da karin zai haddasa za ta kare ne a kan talaka.
Ƙungiyar ta ce ta sha ba gwamnati shawarwari a kan yadda za a inganta rayuwar jama’a amma ta yi biris da su, don haka za ta tattauna da shugabannin rassanta don daukar matakin da ya dace kamar yadda Bbc Hausa ta labarto.