Kungiyar Lauyoyi ta Nijeriya reshen jihar Borno wato NBA, a ranar Asabar ta yi tir da garkame wani Lauya mai suna Sadiq Kachalla, da ‘yan sanda suka yi a Maiduguri.
Shugaban kungiyar na jihar, Muhammad Maigana, ya bayyana wannna garkamewar da aka yiwa Lauyan a matsayin haramtaccen tsarewa, kuma cearsa hakan ya sabawa tsarin kudin mulkin Nijeriya.
Maigana ya bayyana cewa Lauyan ya je ofishin ‘yan sandan ne dake GRA a garin Maiduguri a ranar Juma’a domin ganin an saki wanda yake karewa wanda yake tsare a ofishin ‘yan sandan.
Shugaban NBA din, ya zargi cewa an tsare Lauyan ne bisa umurnin DPO Bulama Usaini na Awa 13 bisa zargin Lauyan ya yi zazzafar muhawara da ‘yan sandan. Shugaban NBA din ya kara da cewa; ‘yan sandan sun ki amincewa su ba da belin Lauyan duk da kokarin hakan da kungiyar ta yi.
Sai dai a lokacin da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar, Edet Okon, ya ce ba shi da labarin wannan zancen, sai dai a cewarsa zai tuntuba domin jin gaskiyar lamarin.SHARE.