Wasu kungiyoyin fararen hula karkashin inuwar ‘Centrum Initiative For Development and Fundamental Rights Advocacy and Advocate Movement’ sun bukaci da a gaggauta hukunta sojoji da sauran wadanda ke da hannu kan kisan ‘Yan Shi’a a Zariya da aka yi a shekarar 2015, domin a cewarsu hakan ya saba wa dokar kasa.
Kungiyoyin sun bayyana hakan ne cikin wata sanarwar da suka fitar a ranar Asabar a Abuja, inda suka nakalto sashe na 33 na dokar kasa, inda suka ce ya bai wa kowanne dan Nijeriya damar rayuwa.
“Dokar kasa ta ce ‘kowanne mutum yana da ikon yin rayuwa, kuma babu wanda yake da ikon katse mishi wannan hakkin, idan dai ba kotu ba ce ta yanke masa hukuncin kisa’ kamar yadda a kundin tsarin kasa da aka yi wa kwaskwarima a 1999.
“Tsakanin 12 zuwa 14 ga watan Disamba, 2015, sojojin kasa na Nijeriya sun kona ‘Yan Shi’a a raye, sun harbe wasu, sun yi wa wasu fyade, sannan kuma sun rushe gidaje, inda daga bisani suka bizne maza da mata a wani kabarin baidaya da suka yi a Mando cikin jihar Kaduna.
“Wadannan laifukan ba za a taba mantawa da su ba a tarihi da kuma kokarin da muke wajen kare hakkin dan adam a Nijeriya,” inji su.
Kungiyar ta kuma koka kan yadda hukumomi ke ci gaba da tsare Shugaban ‘Yan Shi’a, Shaikh Zakzaky da matarsa, Malama Zeenat sabanin umurnin kotu na cewa a sakesu, kuma a biyasu diyyar naira miliyan 50.
“Wadannan laifuka duk sun saba wa dokokin kasashen duniya, ciki har da dokar hana cin zarafi na kasa-da-kasa ta shekarar 2017, wacce ta ke haramci ga cutar da wasu jama’a kan banbancin siyasa, launin fata, kasa, kabila, al’ada ko addini.
“Don haka muke kira a gaggauta hukunta wadanda ke da hannun kan kisan ‘Yan Shi’a; ko sarakunan gargajiya ne kuma ‘yan siyasa ne, ko kuma fararen hula ne kawai su,” a cewar gamayyar kungiyoyin.
Sanarwar na dauke da sa hannun Dakta Hasan Bala, Geoffrey N Nwokolo Esq, Prince Adelaje Adeoye, Kwamared Ecoja Godwin, Dakta Y. B. Abubakar, Kwamared Ahmad Shuaib da Kwamared Mabel Christiana Abba.