Wakiliyarmu Zainab Garba Musa
Gamayyar kungiyoyin fararen hula kan yaki da cin hanci da rashawa karkashin wata cibiya Mai kyamar cin hanci da rashawa wato GLOCCOLOC tayi Allah wadai da irin bayanai da Sarkin Kano Muhammadu Sanusi ya bayar kan zargin Al’mandahana da kudaden masaurata.
A zantawarsu da manema labarai a Abuja a litinin din nan, shugaban kungiyar Dr Nwambu Gabriel, yace ya zuwa yanzu bayanan da aka gabatar sun kasa bisa abinda cibiyar tayi tsammani don haka Sai sukayi Kira wa Sarkin da ya bada gamshashshen bayanai kan wannan batu.
Cibiyar ta Kuma bayyana matsayarta da cewar bayanan da sarki Muhammadu Sanusi ya bayar cewar ya gaji kudi biliyan daya da dubu dari Tara sabanin abinda hukumar yaki da cin hanci ta jahar Kano ta bayyana. bayani ne da bai Kammala Ba, Inji su.
Dr. Nwambu, ya bayyana cewar cibiyar ta kasance tana bibiyar yadda lamuran ke gudana da idon basira a jahar ta Kano kan binciken majalisar masarautar Kano bisa zargin Al mandahana na kudi sama da naira biliyan uku a karkashin jagorancin Mai martaba Malam Muhammadu Sanusi na biyu.
Ya Kuma yi nuni da cewar hukumar karban korafin jama’a da Kuma yaki da cin hanci ta jihar Kano a rahoton ta na farko da ta gabatar a ranar 31 ga mayu 2019 wadda ta mikawa sakataren gwamnatin jihar Kano ana zargin sarkin kan kashe kudin jahar yadda ya ga dama ba tare da bin doka ba.
Bisa wannan cigaba gwamnatin jihar Kano ta Mika wa Sarkin takardar tuhuma domin yin bayani kan zarge-zargen da ake masa wanda daga bisani Sarkin ya sanar da nasa Martanin a jaridar Thisday, kan matsayar Sarkin akan wannan zargi Wanda hakan shine musabbabin shirya wannan taron manema labarai.
Domin Lura da la’akari da cewa Sam Sarkin Bai Amsa Tuhumar da aka aike Masa da Ita Ba Wanda kuma hakan ne ya Bamu kwarin Gwiwar cewa ba shi da ta cewa akan Batun Dan haka muke Kira da ya Amsa Zarge Zargen kawai domin ya hutar da Binkicen, Inji su.