Kungiyar likitocin Nijeriya ta nuna takaicinta kan yadda gwamnatocin Kuros Ribas da Kogi suka hana cibiyar dake yaki da yaduwar cutuka ta Nijeriya, NCDC gudanar da gwaje-gwajen annobar Korona a jihohinsu.
Wannan na zuwa ne bayan da gwamnonin suka yi zargin za a yi amfani da matakin gudanar da gwaje-gwajen wajen shigar musu da cutar.
Yayin zantawa da sashen Hausa na RFI, Dakta Yusuf Abdu Misau, malami a Jami’ar Fasaha ta jami’ar Abubakar Tafawa Balewa dake Bauchi, kuma daya daga cikin kungiyar likitocin Nijeriyar, ya ce bayyana matakin da gwamnonin jihohin na Cross River ta Kogi suka dauka a matsayin kuskure babba.
Dakta Misau ya ce irin haka taso faruwa a Jihar Kano, inda da da fari mafi rinjayen al’ummar garin ke ganin cutar Korona ba ta shiga jihar ba, amma bayan soma aikin tawagar kwararrun likitoci sai labari ya sha bamban, haka zalika ya zargi gwamnonin Kogi da Cross River da sanya siyasa cikin lamarin.