• Mutane bakwai ne aka tabbatar da sun mutu sanadiyar cutar a sannanin yan gudun hijira.
• Mutun 91 suka kamu da cutar a wasu yankuna da ke babban birnin tarayya Abuja.
• Hukumomin gwamnatin Abuja sun tabbatar da mullar cutar.
A yau Alhamis, Hukumomin gwamnatin baban birnin tarayya Abuja, sun tabbatar da mutuwar mutun 7, sanadiyar samun barkewar cutar kwalara a birnin.
Mukaddashin sakataran ma’aikatar lafiya na Abuja Dakta Mohammed Kawu ne ya bayyana wa mane ma labarai hakan, inda ya ce an samu rahoto 91 na barkewar cutar.
Ya Kuma bayyana cewa, mutun bakwai sun mutu a sansanin yan gudun hijira da ke unguwar Wassa na yankin Abuja Municipal.
A cewar Kawo, ba a sami rahoton mutuwa a yankin Bwari da kuma Gwagwalada ba.
Kazalika Kawu ya ce, “Akalla mutun 91 ne aka tabbatar da sun kamu da cutar daga yankuna daban-daban na birnin, inda bakwai daga ciki suka mutu, Amma ban da Gwagwalada da kuma Bwari” inji shi.
KARANTA WANNAN LABARIN: Atiku Dan Kasa ne? Kutu ta Sanya ranar yanke hukunci
Ya kara da cewa, an fara samun rahoton bullar cutar ne a wasu yanku na, tun a watan Mayun shekarar 2021
A karshe Kawu ya bayyana cewa, an fara Samar da kayayyakin kwaji da na Kariya, da magunguna, da kuma kayan aiki na kiwon lafiya, domin dakile yaduwar cutar.