A yau Alhamis ne kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar Kwara dake garin Ilorin ta kori dalibai 29 bisa samunsu da laifin magudin jarabawa.
A cewar Kwalejin, ta dauki matakin ne biyo bayan rahoton kwamitin bincike kan lamarin ya gabatar.
A wata sanarwa dauke da sa hannun babbar mataimakiyar magatakardar kwalejin, Mrs Opadiran Oluwakemi, a madadin magatakardar, Mista Kolawole Sheye Akande, an umarci daliban da abin ya shafa da su gaggauta ficewa daga makarantar.
“Saboda haka, majalisar gudanarwar kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar Kwara ta yi la’akari da rahoton kwamitin dangane da lamarin kuma ta amince da koran ku daga Kwalejin.”
Sanarwar ta kara da cewa, “Saboda haka, ku ba daliban Kwalejin bane, kuma ya kamata ku mika dukkan kadarorin Kwalejin da ke hannunku ga shuwagabannin sashenku ko hukumar da ta dace”.
Idan za’a iya tunawa, Kwalejin a watan da ya gabata ta kori dalibai hudu, tare da yanke wa wasu shida hukuncin maimaita aji, bisa aikata irin wadannan laifin.
Kazalika kwalejin wacce ta zayyana sunayen dukkan daliban da abin ya shafa a lokuta biyu, ta shawarce su da su bi umarnin da aka ba su don kaucewa fuskantar shari’a.