By Abbas Yakubu Yaura
A ranar Laraba ne kwamitin majalisar dattawa mai kula da harkokin cikin gida ya kara yawan alawus-alawus na ciyar da hukumar gidan gyaran hali ta Najeriya daga Naira 450 ga kowane mutum a yanzu, izuwa mafi karancin na naira 1,000 a kowace rana.
Jami’an NCS sun kasance a majalisar dattawa a ranar Laraba domin kare kasafin kudin hukumar na shekarar 2022.
Sun bayar da shawarar a kara alawus din ciyar da abinci a kullum zuwa Naira 750 amma kwamitin daya bayyana adadin a matsayin rashin wadatarsa yasa shi ya kai Naira 1,000 daidai da yanayin tattalin arzikin da ake ciki a halin yanzu.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Kwamitin ya yi alkawarin gudanar da bitar kudin ciyar da fursunoni daga Naira 450 zuwa Naira 1000 a kowace rana.
Wata mamba a kwamitin, Sanata Betty Apiafi, ita ce ta gabatar da kudirin neman karin girma kuma dukkanin mambobin kwamitin sun mara mata baya.
Shugaban kwamitin, Sanata Kashim Shettima, yace akwai fursunoni guda dubu 66,000 a cibiyoyin da ake tsare da su a fadin kasar nan, daga cikinsu guda dubu 47,000 wadanda suke jiran shari’a.
Dan majalisar ya kara da cewa rage cunkoso a wuraren da ake tsare da su ya zama wajibi don mayar dasu wurin zama da kuma gyara fursunonin da gaske.
Comments 1