Daga: Abbas Yakubu Yaura
Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party NNPP ta yi watsi da rahotannin da ke cewa dan takararta na shugaban kasa, Rabiu Kwankwaso, zai tsayar da dan takarar shugaban kasa a 2023 na jam’iyyar Labour, Mista Peter Obi a matsayin mataimakin sa.
A cewar NNPP, ba a taba yin irin wannan tattaunawa ko tuntubar juna ba.
KARANTA WANNAN LABARIN: Wani Gujajjen Fursuna A Imo Ya Hallaka Wata Mata Mai Juna Biyu Bayan Ya Daba Mata Wuka
Sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Dr Agbo Major ne ya bayyana hakan a Abuja, ranar Lahadi.
Ya ce, “NNPP ba ta taba cewa dan takarar shugaban kasa, mai girma, Engr. Dr. Rabiu Musa kwankwaso zai iya yarda Peter Obi na jam’iyyar Labour ya zama mataimakin sa ba.
“Rahoton yaudara ne kuma abin kunya ne ga babbar jam’iyyarmu, Dan takararta na Shugaban kasa, Kwankwaso da miliyoyin magoya bayanta a Najeriya da na kasashen waje, kuma ya bukaci ‘yan jarida da su rika bin diddigin rahotannin su kafin su buga su don gujewa tabarbarewar kasa gabanin babban zabe na 2023.
“A matsayina na jama’a, NNPP ta amince da tattaunawar kawance da Jam’iyyar Labour da za ta karfafa da kuma bunkasa dimokuradiyyar kasa yayin da muke kokarin samar da sabuwar Najeriya wacce jam’iyyar za ta lashe zabe.”
Ya kuma yi nuni da cewa, jam’iyyar NNPP na mutunta ‘yan jarida a matsayin masu sa ido kan al’umma da kuma manyan masu ruwa da tsaki a tsarin dimokuradiyyar Najeriya, don haka ya bukaci su rika bin diddigin rahotannin su a kodayaushe kafin su buga su daidai da ka’idojin aikinsu.
Major ya bayyana kwarin gwiwar cewa tare da kafafen yada labarai, jam’iyyar NNPP “za ta gina al’ummar dimokuradiyya mai karfi, ci gaba da daidaito.”
Comments 2