Mai magana da yawun shugaban kasa Muhammadu Buhari wato Mr Femi Adesina ya Bayyana cewa labarin da ake yadawa cewa jirgin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya hau domin zuwa kasar Amurka ya samu matsala yayin da suke a sararin samaniya, wannan labarin shifcin gizo ne kawai.
Mr Adesina ya kuma Kara da cewa shi kansa ya kasance a cikin mutanen da labarin karya yake ci-gaba da cutarwa, domin kuwa akan ƙaga masa labarin da bai ma san daga Asalin ina ya fito ba, musamman a duk lokutan da suka yi tafiya da shugaban kasa.
Ya bayyana hakan ne yayin bikin kaddamar da wani littafi Mai suna ”Labaran karya 101 kan Endsars” wallafar Muhammad Dahiru Lawal (MD) Wanda ya gudana a PRNigeria dake birnin tarayya Abuja a Jiya Juma’a.
Adesina ya bayyana wasu daga cikin jaridu na Internet da cewa sune ke ci-gaba da rura wutar samar da labaran karya, da suke illa ga harkar yada labarai a Najeriya.
”labaran karya wani abu ne dake illa ga ƙasa dama duniya baki daya, a dan haka akwai bukatar kafafen yada labarai su dinga taka tsantsan wajen neman labari” inji Adesina.
Da yake jawabi a wajen bikin kaddamar da littafin mataimaki ga ministan Shari’a na ƙasa Abubakar Malami SAN kan kafafen yada labarai, kuma malami ga mawallafin littafin Dr. Umar Jibrila Gwandu ya ce labaran karya a koda yaushe ba abinda suke haifarwa face cutar da kasa tare da haifar da rikici tsakanin al’ummar ta.
Daga nan sai ya bukaci ƙwararrun ƴan Jaridu da su cigaba da tabbatar da sahihancin labari kafin su wallafa shi.
Shi kuwa, shugaban kamfanin PRNigeria Mallam Yusha’u Shu’aib wanda kuma shine ya tace littafin, mai shafuka 207 ya ce sun samar da littafin ne domin bayyana irin barazanar da labaran karya ke haifarwa ga al’umma.