Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja ta tabbatar da cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka yi awon gaba da ma’aikatan jami’ar Abuja akalla shida.
A wata sanarwa da kwamishinan ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, Babaji Sunday ya fitar, ya ce ya aike da karin kayan aikin ‘yan sanda na zamani da na yau da kullun zuwa jami’ar Abuja (UNIABUJA) da kuma Karin jami’an Tsaro.
Ya ce ya kuma umurci jami’an da su kula da gidajen ma’aikata da sauran cibiyoyin jami’ar, domin karfafa tsaro, da kuma kare lafiyar jama’ar cikin jama’ar jami’ar da kewayen ta.
Kwamishinan ya kuma cewa, rundunar ‘yan sanda da jami’an rundunar soji ta Bataliyar 176 Guards Battalion sun yi gaggawar tura tawagar su zuwa yankin domin kare Al’uma
“Bincike ya nuna cewa mutane shida (6) ne ake zargi da yin garkuwa da su cikin dajin” in ji shi.
Kazalika ya yi kira ga al’umar yankin da su kwantar da hankulan su, ya jaddada cewa tuni jami’an tsaro na aiki tare da jama’ar yankin wajen ceto wadanda lamarin ya shafa.
Ya kuma bada tabbacin cewa za a kama wadanda suka aikata wannan aika-aika tare da gurfanar da su a gaban kotu.
Comments 1