Ma’aikatar shari’a ta jihar Kogi ta bankado ma’aikatan bogi 268 da ke karbar albashi a babbar kotun jihar, kamar yaddar yadda Daily Trust ta ruwaito
Shugaban kwamitin tantance ma’aikatan, Mai shari’a Mohammed Etsu Umar ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin da yake gabatar da rahoton ga mukaddashin alkalin alkalan jihar, mai shari’a Josiah Joe Majebi, a Lokoja babban birnin jihar.
Kwamitin ya kuma ba da shawarar a dakatar da duk wasu nade-naden ‘ba bisa ka’ida ba a ma’aikatan shari’a na jihar Kogi tsakanin watan Janairun 2021 zuwa Yunin shekarar 2022.
Mai shari’a Umar ya ce rashin sanin ya kamata ya haifar da karuwar darajar ma’aikata ‘astronomy’, wanda hakan ke nuna karin kashi 40 cikin 100 na kudin ma’aikata.
KARANTA WANNAN LABARIN: Zaben 2023: Yankin Arewa Maso Yamma Nada Matukar Mahimmanci Ga Nasarar APC – Dattijo
“Bayan an yi nazari sosai kan sunayen sabbin ma’aikatan da aka dauka daga Janairu 2021 zuwa Yuni 2022, jerin sunayen ma’aikatan da kuma lissafin albashi, an gano cewa ba a iya samun wasu sunayen da ke cikin jerin sunayen ma’aikatan na kotun ba da wasu sauran sassan.
“Saboda haka, alamu ne da ke nuna cewa duk da sunayensu na cikin takardar biyan albashi, ba su da wuraren aiki kuma ba sa aiki a ko’ina a ofisoshin Ma’aikatar” in ji shi.
A cikin jawabinsa, CJ ya ce aikin zai kasance abun da ma’aikatar zata ci gaba dayi, don tabbatar da bin tsari da kuma himma wajen daukar ma’aikata da gudanarwa.
Ya yi alkawarin aiwatar da shawarwarin kwamitin ba tare da bata lokaci ba