Machina ya caccaki Kwamishinan Buni kan ayyana Lawan a Matsayin Ɗan takarar Sanata
Kungiyar Yaƙin Neman Bashir Machina ta caccaki Kwamishinan Muhalli na Jihar Yobe, Sidi Yakubu Karasuwa kan ayyana Sanata Ahmad Lawan a matsayin dan takarar sanata na jam’iyyar All Progressives Congress APC ta Yobe ta Arewa.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Husaini Mohammed Isah ya sanya wa hannu kuma ya mika wa manema labarai.
KARANTA WANNAN LABARIN: Gobarar Tankar Mai Ta Kone Gine-gine 10 A Ogun
Kakakin kungiyar, yayin da yake mayar da martani kan kalaman kwamishinan a wani taron da Gwamnatin jihar Yobe ta shirya domin karrama shugaban majalisar dattawa, Ahmad Ibrahim Lawan a garin Gashu’a.
“Mun damu saboda Sidi Yakubu Karasuwa ya fallasa kansa da gangan, kan rikicin Kujerar Sanatan Yobe ta Arewa.
“A matsayinsa na Muƙarrabin gwamnatin Gwamna Buni, ya kamata Kwamishinan Muhalli ya dauki jerin goyon baya daga wurin shugabansa ta hanyar guje wa duk wani furuci da za a yi masa kallon raba kan jama’a, son zuciya da kuma yaudara,” in ji shi.
A cewar sanarwar, sabuwar dokar zabe wadda ita ce dokar aiki da kuma jagorar gudanar da zabe ba a ko’ina ba ta bayyana cewa kwamishinan muhalli yana da hurumin bayyana wani a matsayin dan takara.
“Musamman, sashe na 33 na waccan dokar ba tare da wata shakka ba ya bayyana yadda za a iya maye gurbin wanda ya cancanta.
“Abin da Sidi ya kamata ya fahimta shi ne cewa ba a yi dokar ba don wasa kawai”, in ji shi.
Yayin da ta bayyana kalaman Sidi a matsayin abin takaici da kuma iya fadada rashin fahimtar juna a cikin jam’iyyar, kungiyar yakin neman zaben ta yi alkawarin ci gaba da zama ‘yan kasa masu bin doka da oda.
A halin da ake ciki Kungiyar Kamfen din Machina ta yi Allah-wadai da kakkausar murya kan matakin da wasu jami’an ‘yan sanda suka dauka na hana wasu magoya bayan Bashir Machina shiga garin Gashu’a domin halartar bikin kaddamar da wani muhimmin aiki na Gwamna Mai Mala Buni a Gashu’a.
“Wannan matakin da kansa ya yi rashin mutunta kundin tsarin mulkin Najeriya wanda ya bai wa kowane dan kasa ‘yancin yin motsi da tarayya.
“Muna kira ga kwamishinan ‘yan sanda na jihar Yobe da ya kira mutanensa su ba da umarni kafin lamarin ya ta’azzara”, kungiyar ta bukaci
A wani labarin kuma:Yan bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mutum 4 A Katsina
Wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wani rukunin gidaje masu tsada a Dutsen Reme na karamar hukumar Bakori a jihar Katsina ranar Juma’a tare da yin garkuwa da mutane hudu.
Daily Post ta ruwaito cewa an yi garkuwa da mutanen ne da misalin karfe 10 na dare a lokacin da ake ruwan sama.