Daga Uzairu Dauda Bunga
Gwamnan jahar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya amince da nada Ali Haruna Abubakar Makoda a matsayin Shugaban Ma’aikatan gidan Gwamnatin jahar.
Da yake nuni da irin gudumawar da ya bayar wajen cigaban jahar Kano da Al’ummar ta baki daya, Gwamna Ganduje ya yabawa Makoda bisa sadaukar dakansa wajen samun nasarar Ganduje a wa’adin mulkinsa na farko daga shekarar 2015 zuwa 2019, sai ya jaddada cewa Ali Haruna Makoda jigo ne a jahar Kano wanda hakan ya bashi damar tafiya dashi a gwamnatinsa karo na biyu.
Da yake bukatarsa ya kasance mai lura da sadaukar dakai, Gwamna Ganduje ya tabbatar da nadin nasa a matsayin cancanta.
Dr Makoda, ya shafe shekaru Tara (9) yana karatun Alqur’ani a tsangayar Malam Sule Mai Bakin karfe a unguwar Hausari, Maiduguri dake jahar Borno inda ya haddace Alqur’ani mai tsarki.
Kwanannan aka karramashi da rawanin Gwani na Alqur’ani daga tsangayar gwani Yahuza da Gwani Dan Zargas. Daga bisani Gwamna Ganduje Khadimul Islam, ya nada Gwani Makoda a babbar kujera.
Gwani Makoda an haifeshi a ranar 2 ga watan Febureru 1966 a karamar hukumar Makoda, bayan kammala karatunsa na firamare da sakandare, yayi karatun diploma a fannin tafiyar da harkokin ilimi daga nan sai ya nausa Jami’ar Bayero dake Kano inda ya samu takardar digiri, sai kuma babbar diploma a Jami’a da kuma digiri na biyu a fannin harkokin kasuwanci duk a Jami’ar Bayero.
Gwani Makoda, ya kasance kwamishinan muhalli na baya bayan nan a gwamnatin Ganduje.
Makoda Dan siyasa ne, da ya zamo zababben Shugaban karamar hukumar Makoda har karo biyu, tsohon zababben Sakataren Jam’iyyar PDP na jahar Kano, tsohon mataimakin Shugaban Jam’iyyar PDP na jahar Kano kuma tsohon babban mai bada shawara kan ayyukan birnin Kano.
Har wa yau, gwani Makoda, ya taba kasancewa mamba a hukumar gudanarwar Asibitin koyarwa na Jami’ar Maiduguri lokacin marigayi Shugaban kasa Umaru Musa ‘Yar Adu’a.
An karrama Dr Makoda da lambar doktorin digiri a Jami’ar All Saint dake Amurka.