Yaron tsohon Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Adamu Atiku Abubakar, ya bayyana cewa mahaifinsa zai sake tsayawa takara a shekarar 2023.
Yaron tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana haka ne a yayin da ya halarci taron taya gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Fintiri murnar cika shekara daya akan mulki.
Yace “a ra’ayina ban ga wani laifi dan mahaifina ya sake tsayawa takarar shugabancin kasar nan, saboda yana gogewa a siyasa kuma ciki da wajen kasar nan, dan haka ina da yakinin zai sake tsayawa”.
https://dimokuradiyya.com.ng/gwamna-fintiri-ya-kara-dokar-garkame-jihar-adamawa/
Ya kara da cewa gwamnatin Fintiri ta bawa kowa mamaki duba da irin halin da ake ciki amma gwamnatin tasa ta yi kokarin cika wasu alkawurukan da ta dauka yayin yakin neman zabe.
Adamu ya kara da cewa dalilin da yasa har yanzu bai tunkari siyasa ba, ya bi shawarar mahaifinsa ne na ci gaba da aiki a fanni daban-daban domin samun gogewa wanda zai zame masa tudun dafawa a yayin da shigo siyasa.
A shirye nake idan har al’ummar jihata suka ga ya dace nazo na mulke su to tabbas zan zo nayi takarar Sanata.