Wata mata mai kimanin shekaru 50 a duniya mai suna Hafsat Aliyu da Yaron ta Babangida Usman, sun fada komar Yan-sanda bayan da aka kama su da laifin yima Ali Haruna, dukan tsiya karshe ma ya sambada lahira.
Lamarin hakan ya faru a ranar 13, ga watan Afurelu 2019, a bayan makarantar Firamarin Shango dake karamar hukumar Chanchaga na jihar Neja.
Usman, yace kwatakwata Babana da mamana basa zaman lafiya ko da yaushe suna cikin fada, saboda irin fushin da Babana yake da shi yasa nayi kokarin temakawa mahaifiya ta ban san zai mutu ba kuskure nayi.
Jami’in hulda da Jamaa na hukumar Yan-sandan Jihar Mohammad Abubakar, ya tabbatar da faruwar hakan kuma yace sun amsa laifin su.
Abubakar, ya ce Usman da mahaifiyar sa sun yima mamacin dukan tsiya Wanda yasa aka tafi da shi Asibitin ‘Ibrahim Badamasi Babangida’ don ceto rayuwar sa amma abun yaci tura.
Yansanda sun ce zaa yi bincike da zarar an kammala zaa tasa keyar su zuwa Kotu don yake musu hukunci.