Daga: Abbas Yakubu Yaura
A kasarin ‘yan majalisar dokokin kasar Somaliya a ranar Lahadi sun amince da nadin majalisar ministocin kasar da gagarumin rinjaye.
An tabbatar da gwamnatin Firaminista Hamza Abdi Barre mai mutane 75 bayan da wasu harsasai suka afkawa wasu unguwannin da ke kusa da fadar shugaban kasa a Mogadishu.
KARANTA WANNAN LABARIN: Dangin Shugaba Buhari Sun Yi Watsi Da Tinubu – Reno Omokri
Kakakin majalisar dokokin, Adan Mohamed Nuur Madobe, ya ce “Kimanin ‘yan majalisa 237 ne, ‘yan majalisa bakwai suka ki amincewa, dan majalisa daya ya ki kada kuri’a, yayin da wasu ‘yan majalisa 229 suka amince da sabbin ministocin, don haka aka amince da su.”
Idan har ba a dauki alhakin kai harin ba, kalubalen tsaro zai kasance kan gaba a ajandar sabuwar majalisar da aka nada.
Majalisar ministocin da ta hada da tsohon mataimakin shugaban kungiyar Al-Shabaab, Mukhtar Robow, wanda aka nuna a hannun dama, ana kuma kiransa da Abu Mansur. An rantsar da shi a matsayin ministan harkokin addini.
“Na gode wa Allah. Kuma na yi matukar farin ciki da cewa ‘yan majalisar sun amince da gwamnatina da shirinta na yin aiki, in Allah Ya yarda,” in ji Faraminista Hamza Abdi Barre.
Baya ga ‘yan ta’addar Al-Shabaab da suka shafe shekaru 15 suna gwabza kazamin yaki da gwamnati da al’ummar Somalia, matsalar yunwa da ta kunno kai kuma za ta kasance daya daga cikin abubuwan da sabuwar majalisar ministocin za ta sa a gaba.
Kafin rikicin Rasha da Ukraine, Somaliya ta shigo da kashi 90% na alkama daga kasashen biyu.
A Mogadishu, kayan abinci da masu ba da agaji na duniya ke bayarwa na raguwa.
Dangane da batun tsaro kuwa, shugaba Hassan Sheikh Mohamoud ya ce kawo karshen tashe tashen hankula yana bukatar fiye da matakin soji.