Kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da ayyuka na musamman ya yi sammacin Ministar Kudi, Misis Zainab Ahmed da ta gurfana gaban mambobinta tare da bayyana makasudin sanya Naira biliyan 206 a cikin kasafin kudin shekarar 2023 na ma’aikatar jin kai.
DIMOKURADIYYA ta rawaito cewa Kwamitin ya bayar da sammacin ne a lokacin da ministar harkokin jin kai, kula da bala’o’i da ci gaban jama’a, Sadiya Farouq ta zo kare kudirin kasafin kudin shekarar 2023 na ma’aikatar ta a ranar Litinin.
KARANTA KUMA An Sami Wani Sabani Tsakanin Ministar Kudi Da Majalisar Dattawa
A yayin tattaunawar, ministar jin kai ba za ta iya baiwa kwamitin cikakken bayanin abin da aka yi niyya yi a kasafin kudinta na Naira biliyan 206 ba.
Ta bayyana cewa asusun ya ninka adadin kudin da aka nema na ayyuka a hukumar raya arewa maso gabas da kuma National Social Safety Net a kasafin kudin shekarar 2022 da ba a fitar da su ba.
A Wani Labarin Kuma Ana Bukatar Tuntubar Masu Ruwa Da Tsaki, Don Dawo Da Martabar Kasar Nan – Atiku
Atiku Abubakar dan takarar shugaban Kasa karkashin inuwar jam’iyyar PDP babbar mai hamayya ya ce domin dawo da kasar nan kan turba ana bukatar tuntubar masu ruwa da tsaki na duk bangarorin kasar.
Atiku ya ce yanzu haka yana cibiyar Ecumenical centre domin tattaunawa da kungiyar kiristoci ta kasa CAN a wani bangare na duba yadda za a magance kalubale da matsalolin da kasar ke fuskanta.