ranar Laraba ne majalisar dattijai ta amince da kafa jami’ar harkokin gona a garin Zuru ta jihar Kebbi, hakan ya samu ne sakamakon kurduri mai lamba SB 686, 2019 da mataimakin jagoran majalisar dattijai, Sanata Bala Ibn Na’Allah, (Sanata mai wakiltar Kebbi ta Kudu ya gabatar wa majalisar. Dokar ta bi dukkan matakan da aka tanada, ta kuma samu albarkacin kwamitin majalisar dattijai mai kula da manyan makarantun Nijeriya da kuma kwamiti mai kula da hukumar TETFUND. Shugaban kwamitin, Sanata Barau I. Jibrin (Sanata daga jihar Kano) ya gabatar wa da majalisar rahoton kwamitin, yayin da kuma Sanata Bassey Akpan ya jadda amincewa da rahoton. Shugaban Majalisar Dakta Bukola Saraki ne ya jagoranci zaman kwamitin, inda ya amince da bukatar kafa jami’ar ba tare da wani bata lokaci ba. A jawabisa a azaure majalisar, Sanata Na’Allah wanda shi ne ya dauki nauyin gabatar da kudurin dokar, ya bayyana cewa, ‘Jihohin Zamfara da Zuru ta jihar Kebbi da wasu bangare na Neja ne za su bayar da gudummawa tare fa amfana da jami’ar saboda dimbin jari da za a samu daga kasashen waje, ina kuma da tabbatacin samar da jama’ar zai yi matukar faranta wa al’ummar yankin rai gaba daya,’ inji shi. Ya kuma mika godiyarsa ga shugaban Majalisar Dattijai, Bukola Dsaraki da sauran abokan aikinsa Sanatoci a bisa goyon bayan da suka samu na samar da dokar. An dai far gabatar da dokar ne a shekarar 2018.