Majalisar Dattijai ta tabbatar da naɗin Farfesa Auwalu Bindawa a matsayin Kwamishina a Hukumar Gudanarwar Hukumar Kula da Sadarwa ta Ƙasa (NCC).
Tabbatar da naɗin shi a ranar Talata, ya biyo bayan dubi da akayi akan rahoton da Kwamitin Majalisar Dattijai yayi akan Sadarwa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Harin Rasha ya lalata Tirken gidan talabijin na Kyiv, in ji Hukumomi a Ukraine
Sanata Yahaya Oloriegbe (Mai Wakiltar Kwara ta Tsakiya) ya gabatar da rahoton a madadin Shugaban Kwamitin Sanata Oluremi Tinubu (Mai Wakiltar Lagos ta Tsakiya).
Oloriegbe a gabatarwar shi yace naɗa Bindawa wanda Shugaban Ƙasa Muhammdu Buhari zai yi, yana dai-dai da sashe na 5(3) dana 8 (1) da kuma na 11 (2) na Dokar Hukumar Sadarwa ta Najeriya doka ta shekarar 2003.
Ya ƙara dacewa, wanda za’a naɗan yana da dukkanin abubuwan da ake bukata ta fannin ƙwarewar sa da Karatun sa a Matsayin Kwamishina a Hukumar Gudanarwar Hukumar Kula da Sadarwa ta Ƙasa.
Ya bayyana cewar binciken da aka yi bai bayyana wani almundahana, ko ba dai-dai ba, daga Mambobin Kwamitin da kuma Kotu.
Daga Ƙarshe, an tabbatar da naɗin shi bayan duba da amincewa akan rahoton Kwamitin.