Majalisar Dattijai ta Najeriya ta zartar da wasu kuɗirai guda biyu domin gina Jami’o’i a Babban Birnin Tarayya, Abuja da Jahar Rivers.
Sune Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Abuja,Abaji, da Jami’ar Tarayya ta Mahalli Koroma/Saakperwa Tai Ogoni, Jahar Rivers.
An dai zartar da ƙudirorin bayan yin dubi akan rahotanni guda biyu da Kwamitin Manyan Makarantu da TETFUND ya gabatar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ƴan sanda sun sake kwance wani bam a mashaya a Kaduna
Mataimakin shugaban Kwamitin Sanata Sandy Onuh dayake gabatar da rahoton a madadin Shugaban Kwamitin, Ahmad Babba Kaita, yace ƙudirin gina Jami’ar Tarayya ta Kimiyya da Fasaha, Abaji, zai cike giɓin da ake dashi na ilmi a bangaren Kimiyya da Fasaha.
A cewar Sanatan, Ƙudirin gina Jami’ar Mahalli zai bayar da Fasaha ga Malamai da masu Son ƙwarewa, Wanda hakan zai sanya a riƙa bada shaidar karatun Digiri, dana biyu dana uku da sauran wasu karatuttuka , da bincike.
Dukkanin ƙudirorin an ƙaddamar dasu, bayan yin dubi akan kwamitin