Majalisar Dinkin Duniya ta ce sau 17 dakarun Janar Khalifa Haftar dake kokarin kwace iko da birnin Tripoli a Libya, ke kai hare-hare kan asibitoci da kuma cibiyoyin kula da lafiya a cikin wannan shekara.
Ofishin Majalisar ya bayyana hakan ne bayan harin baya-bayan nan da Dakarun Haftar suka kai kan babban asibitin Tripoli a ranar Alhamis da ta gabata.
Kakakin ma’aikatar lafiyar kasar Amin al-Hashemi ya tabbatar da harin wanda ya ce ya lalata cibiyar kula da lafiyar da sashen yaki da cututtuka masu yaduwa.
Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana bacin ranta da yadda Dakarun Haftar ke kai hare-hare kan fararen hula wanda ke matukar illa ga duk wani yunkuri na sasanta rikicin kasar.
-RFI Hausa