By Abbas Yakubu Yaura
A ranar Lahadin data gabata ne Majalisar Dokokin Jihar Osun tace ta fara gudanar da bincike kan korafin da ofishin mai binciken kudi na jihar ya shigar gabanta, kan shugaban kula da kudaden kwalejin Ilimin jihar dake Ila, Olanrewaju Oyedeji.
Ta kaddar tuhumar da babban mai binciken kudi na jihar, Folorunsho Adesina ya sanya wa hannu, ya shawarci gwamnatin jihar da ta sanya dokar ta-baci kan sashen bayar da tallafin kudi na hukumar bayan gano wasu makudan kudade a asusun makarantar.
Karafin ta kaddar tuhumar ya bayyana bayanan kuɗi na shekarar 2018 da 2019 na kwalejin a matsayin marasa dogaro.
“Tare da tabarbarewar kudi da aka samu a asusun ajiyar Kwalejin Ilimi ta Jihar Osun Ila-Orangun kamar yadda aka kafa ta hanyar samar da tsarin kudi da sauran wasu dokoki, an shawarci gwamnatin jihar da ta ayyana dokar ta-baci a ma’aikatar kudi ta kwalejin Ilimi ta Jihar Osun Ila-Orangun tun bayan da babban mai binciken kudi ya bankado wasu manyan kura-kurai da ake tafkawa a asusun kwalejin,” inji korafin takardar tuhumar.
Amma da yake mayar da martani game da takardar tuhumar, mukaddashin shugaban kwalejin, Farfesa Jimoh Afolabi, a wata wasika da ya aike wa kwamishinan ilimi; Kakakin majalisar, majalisar dokokin jihar Osun da kuma shugaban kwamitin majalisar dokokin jihar Osun akan asusun gwamnati da aka samu a ranar Lahadin da ta gabata, sun zargi babban mai binciken kudi na jihar