‘Yan Majalisar Wakilan Nijeriya sun sha alwashin gudanar da bincike kan sojoji 365 da suka ajiye aikinsu a lokaci guda saboda zargin rashin jindadin shugabancin Laftanar Janar Tukur Burutai.
Hukumomin sojoji sun tabbatar da cewa dama akan bai wa sojoji masu buƙata ajiye aiki damar yin hakan, a wasu lokacin bayan lokaci. Sai dai`yan majalisar Nijeriya sun musanta hakan, inda suka ce ba a taɓa samun sojojin da yawansu ya kai bataliya guda su kuma yi ritaya a lokaci guda ba.
Hon Muhammad Tahir Monguno babban mai tsawatarwa a majalisar kuma shi ne ya gabatar da kudurin da majalisar ta amince don gudanar da bincike, ya shaida wa BBC cewa matsaloli ne kawai suke tilasta wa sojojin yin murabus.