Kwamitin majalisar wakilan tarayya kan harkokin matasa ya ce babu wani shiri yanzu a kasa na kokarin dakatar da aikin yiwa kasa hidima wato NYSC.
Shugaban Kwamitin Yemi Adaramodu shi ya jaddada haka a birnin tarayya Abuja a ranar Alhamis yayin taron kaddamar da littattafai da ya zo daidai da cika shekara 48 da kafuwar hukumar ta NYSC.
A cewarsa NYSC din ita ce hanya daya tilo dake kawo hadin kai tsakanin yan kasa musamman matasa manyan gobe, don haka babu wani dalili na soke ta.
Da ma dai wani dan majalisa ne mai suna Awaji-Inombek Abiante ya gabatar da kudirin soke aikin yiwa ƙasa hidimar na NYSC wanda kuma tuni ya tsallake karatu na biyu.
Adaramodu ya ce ko wane dan majalisar na damar gabatar da kudiri, to amma abinda kwaryar majalisa ta yanke ahi za a yi amfani da shi.
Manya-manyan mutane a kasar nan sun juya baya wa wannan kudiri da aka shiga na Haramta yiwa kasa hidimar.