Wata kungiyar Musulmi mai suna, ‘Network for Democracy and Development,’ a ranar Litinin ta shawarci gwamnati akan ta kokarta wajen karewa da kuma kula da wadanda aka yiwa fyade.
Hakan ya fito ne a wata sanarwa da shugaban kungiyar, Tajudeen Alabede da kuma jami’in hulda da jama’a na kungiyar, Dr Abdul-Wasi Moshood, suka sanyawa hannu. Inda suka bayyana hauhawar yiwa mata fyade a Nijeriya a matsayin abin damuwa.
Sannan sun yi Allah-wadai da yadda ake yiwa mata fyade, inda suka shawarci gwamnati da ta rika hukunta masu fyaden da tsattsauran hukunci.