Tsohuwar ministar lura da harkokin mata, A’isha Alhassan wacce ta fadi zaben gwamnan jihar Taraba na 2019, ta bayyana cewa ta kammala shirye-shiryen komawa tsohuwar jam’iyyarta na PDP.
A’isha Alhassan ta tsaya takarar gwamnan jihar Taraba a karkashin jam’iyyar UDP a zaben 2019, inda ta samu kuri’u har 14, 651.
Ta koma jam’iyyar UDP ne bayan ta kasa samun tikiti a jam’iyyar APC, jam’iyyar da ta tsaya takarar gwamna a zaben 2015. Inda ta samu kuri’u 275,966, wanda ya ba ta damar zama ta biyu, inda Darius Ishaku na PDP ya lashe zaben a 2015.
Daga
baya, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada ta a matsayin ministar lura da
harkokin mata da ci gaban zamantakewa, amma daga baya ta yi murabus daga
mukaminta.
A’isha Alhassan ta shaidawa ‘yan jarida a ranar Lahadi cewa; bayan zama a
tsakanin masu ruwa da tsaki na UDP a garin Jalingo, ta ce mafi yawan magoya
bayanta dake gundumomi 168 dake Taraba sun nemi da ta koma jam’iyyar PDP.