Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumin Kabir Usman, ya nada mai shari’a Sadiq Abdullahi Mahuta (murabus) ne a matsayin sabon Galadiman Katsina (na 11) kuma Hakimin Malumfashi bayan rasuwar marigayi mai shari’a Mamman Nasir. Sarautar Galadima tana daya daga cikin manyan sarautu a masarautar kasancewar sarautar na daya daga cikin masu zaben sabon sarki. Sauran masu zaben sarkin sun hada da Kauran Katsina, Yandakan Katsina da Durbin Katsina. Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan uwa da abokan arziki sun ciki fadar makil sun hallaci taron don taya shi murnar nadin da aka yi masa, nadin sarautar ya ci karo da nadin wasu saurautun. Sauran wadanda aka nada sun hada da Durbin Katsina kuma Hakimin Mani, Alhaji Umar Babani da kuma Hakimin Kafur kuma Dan Galadiman Katsina, Alhaji Rabe Abdullahi. Wasu da aka yi wa nadin sarautar sun hada da Magajin Radda, Kabir Umar, Magajin Garin Danmusa, Sani Muaazu, Magajin Iyatawa, Hassan Junaidu da Magajin Gobir, Tanimu Kabir, manyan mutanen da suka hallarci taron sun hada da gwamnan Katsina, Aminu Masari, mataimakinsa, Mannir Yakubu, tsohon gwamnan Katsina, Abba Musa Rimi, tsoffin mataimakan gwamna biyu, Tukur Jikamshi da Abdullahi Garba Faskari Sarki Abdulmumin Kabir Usman da ya jagoranci nadin sarautan Galadiman Katsina ya bukaci ya yi aiki tuAkuru domin kare hakkin talakawa da darajar masarautar. Ya yi addu’ar Allah ya kawo sauki kan kallubalen tsaro da ake fama da shi a jihar inda ya ce harkar tsar.