By Abbas Yakubu Yaura
Wadanda suka ci gajiyar shirin ayyuka na musamman guda 774 a jihar Kaduna sun koka kan rashin biyan su alawus-alawus din su.
Ana sa ran za a biya wadanda suka ci gajiyar tallafin Naira 20,000 na tsawon watanni uku wanda shi ne tsawon lokacin shirin.
Matasa da mata da yawansu ya kai 23,000 a fadin kananan hukumomin jihar 23 ne ake sa ran za su shiga cikin shirin.
Wasu sun karbi kudadensu yayin da wasu kuma ba su samu nasu kusan shekara guda ba, suna kuma rokon gwamnatin tarayya data kawo musu dauki.
Wani wanda ya ci gajiyar shirin, Bala Sani, a lokacin da yake jawabi a lokacin bikin ba da tuta ga mahalarta taron 540 da aka zabo daga shiyyoyin sanatoci uku na jihar da hukumar kula da ayyukan yi ta kasa (NDE) ta shirya, yace suna bukatar alawus-alawus don fara harkokin kasuwanci.
Shima wani wanda ya ci gajiyar shirin, Haruna Adamu, wanda shi ne shugaban gudanarwa wadanda suka ci gajiyar Kabala Costain, yace shi ma har yanzu bai samu alawus dinsa na tsawon watanni uku ba.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Da take mayar da martani, mai rikon kwaryar hukumar ta NDE, Madam Victoria W. Dada, tace matsalar ba ta hukumar NDE bace, matsalar bankunansu ne.
Kazalika tace sun dauki sunaye da bayanan wadanda ke da koke tare da mika su hedkwatar kasa domin daukar matakin daya dace.
Tace Babban Horon Kasuwanci zai fadada iliminsu wajen samar da dukiyar da aikin yi ga kansu da yadda za su samar da ra’ayoyin kasuwanci, tsare-tsaren tallace-tallace, tsadar kayayyaki da ayyuka da rahotanni masu yiwuwa, da dai sauransu.