An yi garkuwa da wani babban limamin masallacin Yangoji mai shekara 59 Dake Yankin Kwali na Babban Birnin Tarayyar Abuja, tare da Dan san Abdullahi Abubakar Gbedako da kuma wani mutum Mai Suna Aliyu Usman Abubakar mai shekaru 22, gami da wani yaro Ibrahim Abubakar mai shekaru 11 a gidajen su.
Wani makwabcin Limamin mai suna Shuaibu, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, da misalin karfe 11:47 na dare, yayin da wadanda Maharan suka zo dauke da muggan makamai suka shiga gidan Babban Malamin Daddinin Musuluncin.
Ya ce wasu daga cikin yan bindigan sun tsaya a wasu muhimman Wuraren a yankin Kuma suna ta harbi iska domin. Tsoratarwa, yayin da wasu uku kuma suka tsallaka gidan Limamin ta Katanga.
Ya ce akwai a lamomin harbe-harbe da masu garkuwa da mutane suka yi a cikin harabar gidan, wanda suka kwashe kusan mintuna 30 kafin su yi awan gaba da wadanda abin ya shafa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yan bindiga sun sace Matafiya a Delta
Wani dangin babban limamin da ya so a sakaya sunansa, ya bayyana cewa, Maharan sun tuntube su, kuma sun nemi Naira Milliyan 10 a matsayin kudin fansa kudin fansa kafin sakin mutanen.
Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, DSP Adeh Josephine, ta tabbatar da yin garkuwa da limamin da ‘ya’yansa maza biyu.
Ta ce yayin da ake ci gaba da bincike, jami’an ‘yan sanda da kuma jami’an ‘yan banga suna ci gaba da kokarin ceto wadanda lamarin ya shafa.
“Kwamishanan ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, CP Sunday Babaji, ya kuma bukaci al’ummar yankin Yangoji da su kwantar da hankalinsu tare da bayar da duk wani bayani da zai taimaka wa ‘yan sanda wajen cafke wadanda ake zargin,” inji ta.
Comments 1